Skip to content
1 Korintiyawa 7:20-24

1 Korintiyawa 7:20-24

20
Ya kamata kowa yă kasance a matsayin da yake ciki sa’ad da Allah ya kira shi.
21
Kai bawa ne sa’ad da aka kira ka? Kada wannan yă dame ka, sai dai in kana iya samun ’yanci, sai ka yi amfani da wannan dama.
22
Gama wanda yake bawa sa’ad da Ubangiji ya kira shi, ’yantacce ne na Ubangiji; haka ma, wanda yake ’yantacce sa’ad da aka kira shi, bawa ne na Kiristi.
23
Da tsada fa aka saye ku, kada ku zama bayin mutane.
24
’Yan’uwa, a duk matsayin da mutum yake sa’ad da aka kira shi, sai yă kasance haka a sabuwar dangantakarsa da Allah.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options