Skip to content
1 Korintiyawa 10:6-14

1 Korintiyawa 10:6-14

6
To, waɗannan abubuwa misalai ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.
7
Kada ku zama masu bautar gumaka, yadda waɗansunsu suka zama; kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mutanen suka zauna don su ci su kuma sha, suka kuma tashi suka shiga rawa ta rashin kunya.”
8
Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har a rana guda mutane dubu ashirin da uku a cikinsu suka mutu.
9
Kada mu gwada Kiristi yadda waɗansunsu suka yi, har macizai suka kakkashe su.
10
Kada kuma ku yi gunaguni yadda waɗansunsu suka yi, har mala’ika mai hallakarwa ya hallaka su.
11
Waɗannnan abubuwa sun same su ne, domin su zama abubuwan koyi, aka kuma rubuta su domin a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana.
12
Saboda haka in kana tsammani kana tsaye ne, to, ka yi hankali kada ka fāɗi!
13
Ba jarrabar da ta taɓa samunku, wadda ba a saba yi wa mutum ba. Allah mai aminci ne; ba zai bari a jarrabce ku fiye da ƙarfinku ba. Amma in aka jarrabce ku, zai nuna muku mafita, domin ku iya cin nasara.
14
Saboda haka abokaina ƙaunatattu, ku guje wa bautar gumaka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options