Skip to content
1 Korintiyawa 10:1-5

1 Korintiyawa 10:1-5

1
Ba na so ku kasance da rashin sani, ’yan’uwa, cewa dukan kakannin-kakanninmu sun yi tafiya a ƙarƙashin girgije, dukansu kuma suka bi ta tsakiyar teku.
2
An yi wa dukansu baftisma ga bin Musa a cikin girgije da kuma cikin teku.
3
Dukansu sun ci abincin ruhaniya guda
4
suka kuma sha ruwan ruhaniyan nan guda; gama sun sha daga dutsen ruhaniya nan, wanda ya yi tafiya tare da su, wannan dutsen kuwa Kiristi ne.
5
Duk da haka, Allah bai ji daɗin yawancinsu ba; gawawwakinsu kuwa suka bazu ko’ina a cikin hamada.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options