- English
- King James KJV
- Complete Jewish CJB
- World English WEBM
- Berean Standard BSB
- American Standard ASV
- Geneva GNV
- Young's Literal YLT
- Douay-Rheims DRC
- International
- Shqip ALB
- العربية SVD
- বাংলা BN-IRV
- မြန်မာ Judson
- 简体文 CUV-S
- 繁體中文 CUV-T
- Čeština BKR
- Nederlands STVE
- Français LSG
- Deutsch SCH
- Ελληνικά Vamvas
- ગુજરાતી GU-IRV
- Hausa HCB
- עברית Hebrew
- हिन्दी HCV
- Magyar KAROLI
- Bahasa Indonesia INDO-TB
- Italiano Diodati
- 日本語 Kougo
- 한국어 Korean
- മലയാളം MAL
- मराठी MRCV
- Norsk DNB
- فارسی OPV
- Polski BG
- Português Almeida
- Română Cornilescu
- Русский Synodal
- Español RVG
- Kiswahili Neno
- Svenska SV1917
- Tagalog TAG-ADB
- தமிழ் TCV
- తెలుగు TSA
- ภาษาไทย THAI-KJV
- Українська Ohienko
- Tiếng Việt CADMAN
- Yorùbá YCB
Zabura63
Listen to this chapter
0:00
0:00
Ƙishirwar Allah a jeji
1
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Ƙaunar Allah ta fi rai
3
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Tabbaci ga hukuncin Allah
9
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Reading Width chars
Options
Study Note