Titus 3:3-6
3
A wani lokaci can baya mu ma wawaye ne, marasa biyayya, aka ruɗe mu, sha’awace-sha’awace da kwaɗayi iri-iri suka daure mu, muka yi zaman ƙiyayya da kishi, aka ƙi mu, mu kuma muka ƙi juna.
4
Amma da alheri da kuma ƙaunar Allah Mai Cetonmu suka bayyana,
5
sai ya cece mu, ba saboda abubuwan adalcin da muka aikata ba, sai dai saboda jinƙansa. Ya cece mu ta wurin wankan nan na sāke haihuwa da kuma sabuntawan nan ta Ruhu Mai Tsarki,
6
wanda ya zubo mana a yalwace ta wurin Yesu Kiristi Mai Cetonmu,
Settings