Tsallake zuwa abun ciki
Rut 1:1-5

Iyalin Elimelek Sun Yi Hijira Zuwa Mowab

Rut 1:1-5
1
A kwanakin da mahukunta suke mulki an yi yunwa a ƙasar, sai wani mutum daga Betlehem a Yahuda tare da matarsa da ’ya’yansu maza biyu, suka tafi su yi zama na ɗan lokaci a ƙasar Mowab.
2
Sunan mutumin, Elimelek ne, sunan matarsa Na’omi; sunayen ’ya’yan nan nasu biyu, su ne Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Betlehem ta Yahuda. Suka kuwa tafi Mowab suka zauna a can.
3
To, Elimelek mijin Na’omi ya rasu, aka bar ta da ’ya’yanta maza biyu.
4
Suka auri mata Mowabawa, sunan ɗaya Orfa ɗayan kuma Rut. Bayan sun zauna a can kamar shekara goma,
5
sai Malon da Kiliyon suka mutu su ma, aka kuma bar Na’omi babu ’ya’yanta maza biyu da kuma mijinta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options