Romawa 8:14-17
14
Domin waɗanda Ruhun Allah yake bi da su ne ’ya’yan Allah.
15
Gama ba ku karɓi ruhun da ya mai da ku bayi da za ku sāke jin tsoro ba ne, sai dai kun karɓi Ruhun zaman ɗa. Ta wurinsa kuwa muke kira, “Abba, Uba.”
16
Ruhu kansa yana ba da shaida tare da ruhunmu cewa mu ’ya’yan Allah ne.
17
In kuwa mu ’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
Settings