Skip to content
Romawa 2:1-3

Romawa 2:1-3

1
Saboda haka, kai da kake ba wa wani laifi, ba ka da wata hujja, gama a duk lokacin da kake ba wa wani laifi, kana hukunta kanka ne, domin kai da kake ba wa wani laifi kai ma kana aikata waɗannan abubuwa.
2
Yanzu mun san cewa hukuncin Allah a kan masu aikata waɗannan abubuwa daidai ne.
3
Saboda haka sa’ad da kai mutum kurum, kana ba su laifi, duk da haka kana aikata abubuwan nan, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options