Skip to content
Romawa 2:6-11

Romawa 2:6-11

6
Allah, “Zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikin da ya yi.”
7
Ga waɗanda ta wurin naciya suna yin nagarta suna neman ɗaukaka, girma da rashin mutuwa, su za a ba su rai madawwami.
8
Amma ga waɗanda suke sonkai waɗanda suke ƙin gaskiya suke kuma bin mugunta, akwai fushi da haushi dominsu.
9
Akwai wahala da baƙin ciki ga duk mutumin da yake aikata mugunta, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai,
10
amma akwai ɗaukaka, girma da salama ga duk mutumin da yake aikata alheri, da farko Yahudawa, sa’an nan Al’ummai.
11
Gama Allah ba ya nuna bambanci.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options