Skip to content
Zabura 97:1-9

Zabura 97:1-9

1
Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
2
Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
3
Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
4
Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
5
Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
6
Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
7
Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
8
Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
9
Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options