Skip to content
Zabura 97:1-6

Zabura 97:1-6

1
Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
2
Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
3
Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
4
Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
5
Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
6
Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options