Zabura 81:6-16
6
Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an ’yantar da hannuwansu daga kwando.
7
Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. Sela
8
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
9
Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
10
Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
11
“Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
12
Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
13
“A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
14
da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
15
Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
16
Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Settings