Skip to content
Zabura 80:8-16

Zabura 80:8-16

8
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
12
Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke ’ya’yan inabinsa?
13
Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
14
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options