Skip to content
Zabura 80:14-19

Zabura 80:14-19

14
Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
15
saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
16
An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
17
Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
18
Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
19
Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options