Zabura 80:8-11
8
Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
9
Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
10
Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
11
Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.