Zabura 78:19-25
19
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Settings