Zabura 77:7-9
7
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” Sela