Skip to content
Zabura 76:8-12

Zabura 76:8-12

8
Daga sama ka yi shelar hukunci, ƙasa kuwa ta ji tsoro ta kuwa yi tsit,
9
sa’ad da kai, ya Allah, ka tashi don ka yi shari’a, don ka cece dukan masu shan wahala a ƙasar. Sela
10
Tabbatacce fushinka a kan mutane kan jawo maka yabo, waɗanda suka tsira daga fushinka za su zama kamar rawaninka.
11
Ku yi alkawari wa Ubangiji Allahnku ku kuma cika su; bari dukan ƙasashen maƙwabta su kawo kyautai ga Wannan da za a ji tsoro.
12
Ya kakkarya ƙarfin masu mulki; sarakunan duniya suna tsoronsa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options