Zabura 71:5-8
5
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Settings