Skip to content
Zabura 71:1-4

Zabura 71:1-4

1
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options