Zabura 66:17-20
17
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!