Zabura 63:1-8
1
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Settings