Zabura63
Listen to this chapter
0:00
0:00
1
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Use ← → arrow keys to navigate
Settings
Reading Style
Typeface
Font Size px
Options
Study Note