Zabura 49:6-12
6
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Settings