Zabura 44:17-21
17
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Settings