23
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.