Skip to content
Zabura 44:13-16

Zabura 44:13-16

13
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options