Skip to content
Zabura 38:2-8

Zabura 38:2-8

2
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options