Zabura 35:16-18
16
Kamar marasa sani Allah suna mini riyar ba’a; Suna hararata da ƙiyayya.
17
Ya Ubangiji, har yaushe za ka ci gaba da zuba ido kawai? Ka kuɓutar da raina daga farmakinsu, raina mai daraja daga waɗannan zakoki.
18
Zan yi godiya cikin taro mai girma; cikin ɗumbun mutane zan yabe ka.