Skip to content
Zabura 17:9-14

Zabura 17:9-14

9
daga mugaye waɗanda suke kai mini hari, daga abokan gāba masu mutuwa waɗanda suka kewaye ni.
10
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.
13
Ka tashi, ya Ubangiji, ka yi arangama da su, ka durƙusar da su; ka cece ni daga mugaye ta wurin takobinka.
14
Ya Ubangiji, da hannunka ka cece ni daga irin mutanen nan, daga mutanen duniyan nan waɗanda ladarsu yana a wannan rayuwa ne. Kakan cika yunwan waɗanda kake so; ’ya’yansu suna da isashe suna kuma ajiyar wadata wa ’ya’yansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options