Skip to content
Zabura 17:10-12

Girman kai na abokan gāba

Zabura 17:10-12

Girman kai na abokan gāba

10
Sun rufe zukatansu marar tausayi, da bakunansu suna magana da fariya.
11
Sun sa mini ido, yanzu sun kewaye ni, a shirye suke, su jefa ni a ƙasa.
12
Suna kama da zaki mai yunwan abinci, kamar babban zaki mai fako a maɓuya.

Duba kuma

Sauran wuraren da Nassi ya faɗi haka

  • 1 Sama’ila 2:3

    “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
    daga aya ta 10
  • Zabura 31:18

    Bari a rufe leɓunan ƙarairayinsu, gama da fariya da reni suna magana da girman kai a kan adalai.
    daga aya ta 10
  • Zabura 123:4

    Mun jimre da wulaƙanci daga masu girman kai, reni mai yawa daga masu fariya.
    daga aya ta 10
  • Mattiyu 13:15

    Gama zuciyar mutanen nan ta taurare; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. Da ba haka ba, mai yiwuwa su gani da idanunsu, su kuma ji da kunnuwansu, su gane a zuciyarsu, su kuwa juya, in kuma warkar da su.’
    daga aya ta 10
  • Ru’uya ta Yohanna 13:5

    Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
    daga aya ta 10
  • Ru’uya ta Yohanna 13:6

    Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
    daga aya ta 10
  • Karin Magana 6:13

    wanda yake ƙyifce da ido, yana yi alama da ƙafafunsa yana kuma nuni da yatsotsinsa,
    daga aya ta 11
  • Karin Magana 6:14

    wanda yake ƙulla mugunta da ruɗu a cikin zuciyarsa, kullum yana tā-da-na-zaune-tsaye
    daga aya ta 11
  • Zabura 37:14

    Mugaye sukan zare takobi su ja baka don su kashe matalauta da masu bukata, don su kashe waɗanda hanyoyinsu daidai suke.
    daga aya ta 11
  • Zabura 7:2

    in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
    daga aya ta 12
  • 2 Bitrus 2:18

    Gama suna surutai banza na girman kai, ta wurin son bin fasikanci na mutuntaka, sukan jan hankulan mutanen da suke kuɓucewa daga waɗancan masu zama cikin kuskure.
    daga aya ta 10
  • Ayyukan Manzanni 28:27

    Gama zuciyar mutanen nan ta yi tauri; da ƙyar suke ji da kunnuwansu, sun kuma rufe idanunsu. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta a zukatansu, su kuma juyo, in kuwa warkar da su.’
    daga aya ta 10
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options