Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 139:13-18

Allah Ya Halicce Mu Cikin Tsoro da Al’ajabi

Zabura 139:13-18
13
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options