Skip to content
Zabura 139:19-24

Zabura 139:19-24

19
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options