Tsallake zuwa abun ciki
Zabura 135:8-12

Ayyukan Allah Masu Ƙarfi na Ceto

Zabura 135:8-12
8
Ya kashe ’ya’yan fari na Masar, ’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options