Skip to content
Zabura 132:1-10

Zabura 132:1-10

1
Waƙar haurawa. Ya Ubangiji, ka tuna da Dawuda da kuma dukan irin wuyan da ya jimre.
2
Ya yi rantsuwa ga Ubangiji ya kuma yi alkawari ga Maɗaukaki na Yaƙub cewa,
3
“Ba zan shiga gidana ko in kwanta a gado ba,
4
ba zan ba wa idanuna barci ba, ba gyangyaɗi wa idanuna,
5
sai na sami wuri wa Ubangiji, mazauni domin Maɗaukaki na Yaƙub.”
6
Mun ji haka a Efrata, muka yi ƙaro da shi a filayen Ya’ar,
7
“Bari mu tafi wurin zamansa; bari mu yi sujada a wurin sa ƙafafunsa,
8
ka tashi, ya Ubangiji, ka kuma zo wurin hutunka, kai da akwatin alkawarin ƙarfinka.
9
Bari a suturta firistocinka da adalci; bari tsarkakanka su rera don farin ciki.”
10
Saboda Dawuda bawanka, kada ka ƙi shafaffenka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options