1
Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
2
sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
3
Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
4
Amma Ubangiji mai adalci ne; ya ’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.