Zabura 129:5-8
5
Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
6
Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
7
da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
8
Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”
Settings