Zabura 124:5-8
5
Da ruwa mai hauka ya share mu ƙaf.
6
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda bai bari aka yayyage mu da haƙoransu ba.
7
Mun tsira kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta; an tsinke tarko, muka kuwa tsira.
8
Taimakonmu yana a sunan Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa.