Skip to content
Zabura 119:9-16

Zabura 119:9-16

9
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options