Zabura 119:145-149
145
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Settings