Zabura 118:5-14
5
Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin ’yantar da ni.
6
Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
7
Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
8
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
9
Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
10
Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
11
Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
12
Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
13
An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
14
Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Settings