Zabura 106:35-39
35
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37
Suka miƙa ’ya’yansu maza hadaya ’yan matansu kuma ga aljanu.
38
Suka zub da jini marar laifi, jinin ’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Settings