Zabura 105:37-41
37
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Settings