Skip to content
Karin Magana 3:13-26

Karin Magana 3:13-26

13
Mai albarka ne mutumin da ya sami hikima, mutumin da ya sami fahimi,
14
gama ta fi azurfa riba tana kuma da amfani fiye da zinariya.
15
Ta fi lu’ulu’u daraja; ba a kwatanta abin da ka fi sha’awa da ita.
16
Tsawon rai yana a cikin hannunta na dama; a hannunta na hagu kuwa akwai arziki da bangirma.
17
Hanyoyinta hanyoyi ne masu daɗi, dukan hanyoyinta kuma salama ne.
18
Ita itacen rai ne ga waɗanda suka rungume ta; waɗanda suke riƙe da ta za su zama masu albarka.
19
Ta wurin hikima Ubangiji ya kafa harsashin duniya, ta wurin fahimi ya shirya sammai inda suke;
20
ta wurin sani aka rarraba zurfafa, gizagizai kuma suka zubo raɓa.
21
Ɗana, ka riƙe sahihiyar shari’a da kuma basira, kada ka bar su su rabu da kai;
22
za su zama rai a gare ka, abin adon da zai gyara wuyanka.
23
Sa’an nan za ka bi hanyarka lafiya, ƙafarka kuwa ba zai yi tuntuɓe ba;
24
sa’ad da ka kwanta, ba za ka ji tsoro ba; sa’ad da ka kwanta, barci zai yi maka daɗi.
25
Kada ka ji tsoron masifar da za tă faru farat ɗaya ko lalacin da yakan auka wa mugaye,
26
gama Ubangiji zai zama ƙarfin halinka zai kuwa kiyaye ƙafarka daga fāɗawa a tarko.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options