Skip to content
Karin Magana 18:9-13

Karin Magana 18:9-13

9
Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
10
Sunan Ubangiji hasumiya ce mai ƙarfi; masu adalci kan gudu zuwa wurinta don su zauna lafiya.
11
Dukiyar masu arziki ita ce birninsu mai katanga; suna gani cewa ba za a iya huda katangar ba.
12
Kafin fāɗuwarsa zuciyar mutum takan yi girman kai, amma sauƙinkai kan zo kafin girmamawa.
13
Duk wanda yakan ba da amsa kafin ya saurara, wannan wauta ce da kuma abin kunya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options