Karin Magana 18:6-9
6
Leɓunan wawa kan jawo masa faɗa, bakinsa kuma kan gayyaci dūka.
7
Bakin wawa lalatar da kansa yake yi leɓunansa kuma tarko ne ga ransa.
8
Kalmomin mai gulma kamar abinci mai daɗi suke; sukan gangara zuwa can cikin gaɓoɓin mutum.
9
Wanda yake ragwanci a aikinsa ɗan’uwa ne ga wanda yakan lalatar da abubuwa.
Settings