Skip to content
Karin Magana 10:22-32

Karin Magana 10:22-32

22
Albarkar Ubangiji kan kawo wadata, ba ya kuma ƙara wahala a kai.
23
Wawa yakan ji daɗi halin mugunta, amma mutum mai fahimi kan ji daɗin hikima.
24
Abin da mugu ke tsoro shi ne zai same shi; abin da adali ke bukata yakan sami biyan bukata.
25
Sa’ad da hadiri ya taso, yakan watsar da mugaye, amma adalai za su tsaya daram har abada.
26
Kamar yadda ruwan tsami yake ga haƙora hayaƙi kuma ga idanu, haka malalaci yake ga wanda ya aike shi.
27
Tsoron Ubangiji kan ƙara tsawon rai, amma akan gajartar da shekarun mugaye.
28
Abin da adali yake sa rai yakan kai ga farin ciki, amma sa zuciyar mugu ba ya haifar da kome.
29
Hanyar Ubangiji mafaka ce ga adalai amma lalaci ne ga waɗanda suke aikata mugunta.
30
Ba za a taɓa tumɓuke masu adalci ba, amma mugaye ba za su ci gaba da kasance a ƙasar ba.
31
Bakin adalai kan fitar da hikima, amma za a dakatar da mugun harshe.
32
Leɓunan adalai sun san abin da ya dace, amma bakunan mugaye sun san abin da yake mugu ne kawai.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options