Skip to content
Karin Magana 1:24-33

Karin Magana 1:24-33

24
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options