Nehemiya 12:12-26
12
A kwanakin Yohiyakim, waɗannan su ne shugabannin iyalan firistoci, na iyalin Serahiya, Merahiya; na iyalin Irmiya, Hananiya;
13
na iyalin Ezra, Meshullam; na iyalin Amariya, Yehohanan;
14
na iyalin Malluk, Yonatan; na iyalin Shebaniya, Yusuf;
15
na iyalin Harim, Adna; na iyalin Merahiyot, Helkai;
16
na iyalin Iddo, Zakariya; na iyalin Ginneton, Meshullam;
17
na iyalin Abiya, Zikri; na iyalin Miniyamin da na Mowadiya, Filtai;
18
na iyalin Bilga, Shammuwa; na iyalin Shemahiya, Yehonatan;
19
na iyalin Yohiyarib, Mattenai; na iyalin Yedahiya, Uzzi;
20
na iyalin Sallu, Kallai; na iyalin Amok, Eber;
21
na iyalin Hilkiya, Hashabiya; na iyalin Yedahiya, Netanel.
22
Shugabannin iyalin Lawiyawa a kwanakin Eliyashib, Yohiyada, Yohanan da Yadduwa, da kuma na firistoci, an rubuta su a zamanin mulkin Dariyus mutumin Farisa.
23
Shugabannin iyali cikin zuriyar Lawi har zuwa lokacin Yohanan ɗan Eliyashib, an rubuta su a cikin littafin tarihi.
24
Shugabannin Lawiyawa kuwa su ne Hashabiya, Sherebiya, Yeshuwa ɗan Kadmiyel, da ’yan’uwansu, waɗanda suka tsaya ɗaura da su don su yi yabo da kuma godiya, sashe ɗaya kan ba da amsa ga ɗaya sashen, kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta.
25
Mattaniya, Bakbukiya, Obadiya, Meshullam, Talmon da Akkub su ne matsaran ƙofofi waɗanda suka yi tsaron ɗaukan ajiya a ƙofofi.
26
Sun yi hidima a kwanakin Yohiyakim ɗan Yeshuwa, ɗan Yozadak, kuma a kwanakin Nehemiya gwamna da kuma na Ezra firist da kuma marubuci.
Settings