Skip to content
Mattiyu 8:18-22

Mattiyu 8:18-22

18
Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
19
Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
20
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
21
Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
22
Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options